Gwamna Radda Ya Nada Tanimu Gambo A Matsayin Kwamishina Mai Kula Da Ma’aikatar Kananan Hukumomi

top-news


Katsina Times- 28 ga Agusta, 2024 - Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya nada Hon. Bashir Tanimu Gambo a matsayin Kwamishina Mai Kula Da Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu.

An yi wannan nadin ne a matsayin matakin rikon kwarya yayin da ake jiran nada kwamishina na dindindin ga ma’aikatar, wadda ta zama babu kowa a kai bayan nadin Farfesa Badamasi Lawal Charanci a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Shirin Tallafin Jama’a ta Kasa (NSIPA) daga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Hon. Gambo, wanda a halin yanzu shi ne Kwamishinan Kudi, ya nuna kwarewar sa a harkokin kananan hukumomi, inda ya rike mukamin Shugaban Karamar Hukumar Dutsinma daga 2008 zuwa 2011.

Gwamna Radda ya nuna gamsuwa da kwarewar Hon. Gambo wajen jagorantar ma’aikatar tare da ci gaba da gudanar da ayyukansa na Kwamishinan Kudi.

Gwamnatin ta tabbatar wa al’umma cewa ana kan aiwatar da tsarin nada kwamishina na dindindin ga Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, kuma za a kammala hakan nan ba da jimawa ba.

NNPC Advert